Raba a Facebook
Tura zuwa Twitter
Wata babbar kotun jihar Kano karkashin jagoramcin Mai Shari’a Abdu Maiwada Abubakar ta haramta wa Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ismaila Dikko da wani Sufeta mai suna Friday kama wani shahararren dan jarida, Nasiru Salisu Zango.
Dan jaridar a cikin shirin mai suna “In Da Ranka” a gidan rediyon Freedom ya bankaɗo yadda wasu jami’an ‘yan sanda ke karbar miliyoyin naira daga hannun wadanda ba su ji ba ba su gani ba da sunan beli.
-
Facebook
Twitter