MARABA DA SHEKARAR 2022: Shekarar da tsadar fetur da harajin jiki magayi za su yi wa ‘yan Najeriya lilis

A ƙarshen 2021 Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta jefa ‘yan Najeriya cikin tunanin irin mawuyacin halin da za a shiga a shekarar 2022.

Yayin da Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed ta bayyana cewa a cikin 2022 za a bijiro da sabbin hanyoyin tatsar kuɗaɗen haraji a ƙasar nan, a ɓangaren man fetur kuma gwamnati cewa ta yi za ta cire tallafi.

Idan an cire tallafin kuwa, da kan ta cewa ta yi farashin litar mai za ta iya kaiwa naira 340.

Tsarabar 2022: Gwamnatin Buhari Za Ta Tsula Farashin Litar Fetur, Amma Za A Riƙa Biyan Talakawa Naira 5000 Su Rage Raɗadin Ƙuncin Rayuwa

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za ta cire kuɗin tallafin man fetur, wanda hakan na nufin za a ƙara kuɗin litar fetur.

Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed ce ta bayyana haka, a lokacin ƙaddamar da wani shiri na Bankin Duniya a Najeriya.

Sai dai kuma ta ce gwamnatin tarayya za ta zaƙulo mutane miliyan 30 zuwa 40 da su ka fi kowa talauci a kasar nan ta riƙa ba su naira 5,000 kowace Wata, domin rage masu raɗaɗin ƙuncin rayuwar da za su iya afkawa a ciki nan gaba idan an ƙara wa fetur farashi.

Ta ce rarar kuɗaɗen da za a riƙa samu ce za a duba sannan a san ko adadin mutum nawa ne za su riƙa amfana da tallafin.

Idan ba a manta ba, Bankin Bada Lamuni na Duniya, IMF ya shawarci Najeriya ta gaggauta cire tallafin mai domin ta ƙara samun kuɗin shiga. Kuma ta rage kashe kuɗaɗe a ayyukan da ba masu muhimmanci ba.

Bankin IMF ya shawarci Najeriya ta gaggauta cire tallafin da na kuɗin wutar lantarki a farkon 2022:

Idan Gwamnatin Najeriya ta yi amfani da shawarar Bankin Bada Lamuni na Duniya (IMF) har ya cire tallafin man fetur da na wutar lantarki a farkon 2022, ‘yan ƙasar nan za su shiga sabuwar shekara cikin halin ƙuncin rayuwar da ta fi ta shekarar 2021 da ake ciki.

Kai tsaye ba wani abu ba ne cire tallafin man fetur da na wutar lantarki, ma’ana ita ce a ƙara wa farashin litar man fetur da wutar lantarki kuɗi.

IMF ta gargaɗi Najeriya cewa yawan kuɗaɗen da ta ke kashewa idan auna su da waɗanda ta ke samu, to za’a ci gaba da samu wawakeken giɓi a kowace shekara, kamar irin wanda aka samu a bana cikin 2021, to haka ma za ta kasance a shekara mai zuwa.

“Amma idan aka cire tallafin fetur da na kuɗin lantarki, an kamo hanyar saisaita matsalolin ƙaranci kuɗi a hannun gwamnati kenan.

“Amma kuma tilas sai ita gwamnatin ta bijiro wasu tsare-tsaren da za ta rage wa talakawa tsadar rayuwa, sakamakon matsin da za su shiga idan an ƙara kuɗin fetur da kuɗin wutar lantarki. Kuma dama akwai wannan sharaɗin a cikin Sabuwar Dokar Man Fetur ta 2021 cikin watannin baya.”

IMF ya ƙara da cewa, tafiyar-hawainiyar da sabon tsarin canjin kuɗaɗe ke yi, tare da rashin tabbas na kasa maido maƙudan kuɗaɗen da ɓarayin gwamnati su ka sace suka ɓoye a waje, ya rage ƙarfin yawan shigowar jari mai nauyi a Najeriya.”

Wasu ƙarin matsalolin da tattalin arzikin Najeriya ke ci gaba da fuskanta, a cewar IMF, sun haɗa da ƙarancin kayan da Najeriya ke fitarwa waje.

A kan haka sai IMF ta nemi Najeriya ta fito da wani tsari da zai daɗe tsawon lokaci ya na hana kuɗaɗen ajiyar Najeriya a waje raguwa.

Jiki Magayi: Gwamnatin Buhari za ta bijiro da ƙarin sabbin hanyoyin karɓar haraji cikin 2022 -Inji Ministar Kuɗaɗe.

Duk da halin ƙaƙa-ni-ka-yin da ‘yan Najeriya ke ciki na ƙuncin rayuka da rashin tsaro, Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed ta bayyana cewa akwai yiwuwar gwamnatin tarayya ta fito da sabbin hanyoyin karɓar haraji cikin shekarar 2022, mai kamawa nan da bayan makonni biyu.

Zainab ta ce akwai buƙatar ƙarin samun kuɗaɗen haraji domin ƙara wa daɓe makuba, tunda a cewar ta, “yanzu tattalin arzikin Najeriya ya hau miƙaƙƙar hanya da babu karkata ko waskiya.”

Zainab ta fitar da wannan furuci a lokacin da ta ke wa masu ruwa da tsaki jawabi wurin sauraren Kudirin Dokar Kuɗaɗe ta 2021, taron da Kwamitin Majalisar Tarayya kan Harkokin Kuɗaɗe ya shirya a ranar Litinin, a Abuja.

Ta ce a cikin ƙudirin an gabatar da shawarwarin gyare-gyare, inda ta ce kuma wasu harajin ma za a ƙara fito da su a cikin tsakiyar shekarar 2022 ɗin.

“Mu na nan mu na shirin bijiro da sabbin ƙudirori a tsakiyar 2022.” Inji Zainab.

Sai dai kuma ta ce Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ta kauda kai daga yin magana kan Harajin ‘VAT’ da na ‘La’ada Waje’, saboda batutuwan su na kotu, saboda wasu sun shigar da gwamnatin tarayya ƙara a kan harajin biyu.

Idan ba a manta ba, Jihar Ribas ta yi nasara a Kotun Tarayya cewa ita ke da alhakin karɓar harajin VAT ba tarayya ba, lamarin da Gwamnatin Tarayya ta ɗaukaka ƙara.

Jiki Magayi: Tulin Hanyoyin Harajin Da Za A Bijiro Cikin 2022:

“Tuni mun tsara ƙudiri da daftarin yi wa dokokin kuɗaɗe kwaskwarima domin ƙara danƙara haraji a ƙasar nan. Musamman a ɓangaren harajin cikin gida, tsarin tasarifin kuɗaɗen harajin, sai kuma harajin da ake karɓa daga kayayyakin da ake shigowa da su daga waje, sai harajin gyaran tsarin karɓar harajin da kuma tsarin yadda gwamnati ke sarrafa kuɗaɗen harajin.

“Akwai daftarin gyaran Dokar Masu Manyan Hannayen Jari, Dokar Harajin Kuɗaɗen Shigar Kamfanoni, Dokar Kafa Hukumar Tara Haraji ta Tarayya (FIRS), Dokar Harajin Kuɗaɗen Shigar Ɗaiɗaikun Mutane, Dokar Harajin La’ada Waje, Dokar Harajin Jiki Magayi da sauran su._