LALACEWAR TSARO A KATSINA: Kowa ya kare kan sa, wanda ya mutu ya yi shahada – Gwamna Masari

Kusan shekaru bakwai bayan hawa mulkin Shugaba Muhammadu Buhari, ɗan Jihar Katsina, rashin tsaro na ƙara dagulewa a jihar sa ta haihuwa, har ta kai ga Gwamna Aminu Masari ya umarci ɗaukacin ‘yan jihar cewa kowa ya sayi bindigogin kare kan sa daga ‘yan bindiga.

Da ya ke jawabi, Masari ya ƙara jaddada cewa jami’an tsaro su kaɗai ba za su iya magance wannan gagarimar matsala ba.

Da ya ke zantawa da manema labarai a Gidan Gwamnatin Katsina mai suna Muhammadu Buhari House, Masari ya ce jami’an tsaro sun yi ƙaranci matuƙa, ta yadda yawan su ba zai iya daƙile ‘yan bindiga ba.

“Musulunci ma ya yarda mutum ya kare kan sa. Tilas mutum ya tashi ya kare kan sa, ya kare iyalin sa da dukiyar da. Idan ka mutu wajen kare kan sa ko iyalin ka ko wata dukiyar ka, to an kyautata maka cewa ka mutu shahidi.

“Abin mamaki ne a ce ɗan bindiga ya mallaki bindiga, shi kuma mutumin ƙwarai mai ƙoƙarin kare kan sa da iyalin sa a ce ba shi da bindiga.” Haka Masari ya bayyana.

Masari ya ce gwamnatin jiha za ta taimaki waɗanda ke so su mallaki bindiga da nufin kawo ƙarshen wannan matsalar tsaro.

“Za mu goyi bayan masu halin da su ka bijiro domin su taimaka wa al’umma su mallaki bindigogi.

“Lokacin da Shugaba Muhammadu Buhari ya zama shugaba, ya yi ƙoƙarin ƙara yawan jami’an tsaro. Amma duk da haka ba su wadata ba.

“Ku lissafa, ‘yan sanda nawa mu ke da su a ƙasar nan? Sojojin ƙasar nan dududu guda nawa ne?

“Kai ko ma cewa aka yi kowane ɗan sanda ya koma jihar sa, hakan ba zai magance matsalar ba. Saboda haka idan mu ka riƙe hannu mu ka ce mu zura ido, to kan mu kawai za mu ƙwara.” Inji Masari.

Masari ya bada shawara cewa aikin ‘yan sanda ne su yi rajistar bindigogin da fararen hula za su saya, domin su tabbatar da cewa an yi aikin da ya dace da su.