KUSKURE: Ba da gangar Tinubu ya ce El-Rufai ya maida Kaduna ƙazamin birni daga ruɓaɓɓen birni ba – Onanuga

Yayin da Tinubu ke bai wa Gwamna Nasiru El-Rufai shawarar kada ya zubar da makaman siyasa a 2023 ya yi ritaya kamar yadda ya taɓa bayyanawa, Tinubu ya kwafsar inda ya yabi ayyukan raya ƙasa da El-Rufai ya yi, a ƙoƙarin yabon sa, sai ya ɓata rawar sa da tsalle.
“Ba za mu bari ka gudu daga siyasa ko mulki ba. Irin namijin ƙoƙarin da ka yi inda ka maida Kaduna ruɓaɓɓen birni zuwa ƙazamin birni, ya nuna cewa kai abokin tafiya ne…”
Sai dai kuma kakakin kamfen ɗin Tinubu Bayo Onanuga ya bayyana cewa kuskure harshe ne Tinubu yayi, kuma ba abu ne sabo ba, ana iya samun haka daga ko ma waye.
” Tinubu mutum ne shima zai iya yin kuskuren harshe a lokacin furta magana. Abinda ya ke nufi shine daga abu mara kyau zuwa abu mai kyau, kuma mutanen da suka halarci taron sun fahimce shi sarai garau.
” Abin kawai siyasa ce wasu suka maida shi, duk sun dira kafafen yanar gizo suna ta surutai.