KADUNA TA DAGULE: Yadda ‘yan Bindiga suka kashe mutum 9, suka ji wa wasu rauni – Kwamishina Aruwan

Kwamishinan tsaron jihar Kaduna Samuel Aruwan ya bayyana cewa ‘yan bindiga sun kashe mutum 9 sannan sun ji wa biyu sun ji rauni a kananan hukumomin Chikun, Zaria, Igabi da Zangon Kataf.

Aruwan ya kara da cewa gwamnati ta samu labarin haka ne daga bayanan da jami’an tsaro dake aiki a jihar suke sanar mata.

Aruwan ya ce ‘yan bindiga sun kashe mutum uku a kauyen Buruku-Udawa a dalilin rufe hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari da suka yi a karamar hukumar Chikun.

“Maharan sun kashe Umma Ibro-Kontagora, Abdullahi Noma-Kontagora da wani da ba a san sunan sa ba sannan Jamilu Kafinta Udawa ya samu raunin harsashi a jikinsa kuma yana kwance a asibiti.

“A kauyen Yola-Kadi ‘yan bindiga sun kashe Danjuma Maiungwa, mutum daya ya ji rauni.

A kauyen Sako dake karamar hukumar Zangon Kataf ‘yan bindiga sun kashe Samson Maza da David Garba.

“Jami’an tsaro sun tsinci gawar mutum biyu a kauyen Kurfi-Magamiya inda bayan bincike aka gano cewa gawarwakin Nehemiah Abba da Samuel Gwazah ne.

A karamar hukumar Zaria ‘yan bindiga sun kashe Alhaji Habibu a kauyen Saye.

Kwamishina Aruwan ya yi alhinin rasuwar wadanda aka kashe sannan ya ce gwamnati za ta ci gaba da samarwa mutanen jihar tsaro duk da matsalolin da ake samu.