Gwamnatin Najeriya ta sanar da dakatar da ayyukan shafin Tiwita a Najeriya.
Wannan sanarwa na kunshe ne a wata takarda wanda ta fito daga ofishin ministan yada labarai, Lai Mohammed.
Lai Mohammed ya ce gwamnati ta dakatar da ayyukan tiwita a kasar nan ne saboda shafin na neman kawo rudani da wargaza hadin kai da tsaro a kasar nan..