Buhari ya yi abinda na ga cewa komawa APC ne kawai zan yi in saka masa – In Ji Fani Kayode

Tsohon ministan Sufurin Najeriya kuma jigo a jam’iyyar PDP a da, ya bayyana cewa yadda zai iya saka wa irin Nasarorin da gwamnatin Buhari ta samu kenan dawowa da jam’iyyar APC da yayi.

Idan ba a manta ba Fani-Kayode ya koma jam’iyyar APC a yau Alhamis inda bayan haka suka dunguma suka garzaya fadar shugaban kasa domin a yi masa wankar tsarki.

Gwamnan Jihar Zamfara Bello Matawalle, Sakataren gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha da Shugaban riko na jam’iyyar Mala Buni suka raka Fani Kayode fadar shugaban Kasa.

A jawabin da yayi wa manema labarai a fadar shugaban kasa, Kayode ya bayyana cewa ya dawo jam’iyyar APC ne saboda ya hada hannu da gwamnatin Buhari domin ci gaban Kasa.

” Buhari ya taka rawar gani a kasar nan musamman a fannin harkar samar da tsaro. Wannan ya sa dole ire-iren mu mu zo mu hadu wuri daya domin a ci gaba da samun nasara a abubuwan da gwamnati ta sa a gaba.

” Ita dama siyasa haka ta gada, duk inda kaga nan ne ci gaba ya karkata ga toh a matsayin ka na dan kasa, idan har kana da kishin kasa, sai ka zo a hadu wuri guda domin ci gaban kasar.

Gwamnan Yobe Mala Buni ya bayyana cewa, shugaba Buhari ya yi matukar Farin cikin wannan gagagimin kamun da APC ta yi.