RASHIN TSARO: Halin da Jihar Neja ke ciki daidai ya ke da zamanin yaƙin ‘ƙatilan-maƙatulan’ – Gwamna Bello

Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Bello ya bayyana cewa halin da Jihar Neja ke ciki ya yi munin da babu wani bambanci da zamanin yaƙin ‘ƙatilan maƙatulan’, ya ce ya kamata a san cewa yaƙi fa ake yi a Neja.

Bello ya nuna bacin ran sa ne domin ƙara sanar da halin kashe-kashe da hare-haren da ‘yan bindiga ke yi a Neja, tare kuma da sake yin kira ga Gwamnatin Tarayya domin ta kai wa Jihar Neja ɗaukin gaggawa.

Bello ya yi maganar ce ganin yadda hare-hare su ka yi yawa a Ƙananan Hukumomin Rafi, Wushishi da Lavun. Ya ce an kai munanan hare-haren a garuruwan Wushishi, Tegina da Batati.

“Lamarin fa ya yi muni fiye da yadda duk ake tsammani. Maganar gaskiya mun afka zamanin yaƙe-yaƙe. Kuma kamata ya yi a tunkari matsalar nan gadan-adan ba tare da bata lokaci ba.”

Haka Kakakin Gwamnan, Mady Noel-Berje ta bayyana cewa Gwamna Abubakar ya faɗa, cikin wata sanarwa da ta sa wa hannu a madadin gwamnan.

Ya ce za a fara bi gida-gida domin a tabbatar da yawan yara ƙananan da aka sace, aka yi garkuwa da su.

Jami’in gwamnati ya ce ‘yan bindiga kamar su 70 ne su ka karaɗe ƙauyuka 17, a cikin ƙaramar hukumar Wushishi, inda su ka harbi mutane da dama.

An kuma tabbatar da cewa ruwa ya tafi da mata da ƙananan yara, a lokacin da su ka tinjima cikin Kogin Kaduna, domin su tsira daga ‘yan bindiga.

Mutanen da ake nema ba a san inda su ke ba a halin yanzu, ‘yan garuruwan Babako ne da Tashan Jirgi, Kwakwagi,Fakars, Ndiga, Buzu, Akare, Kala Kala, Agwa, Anguwan Gizo, Tsamiya da sauran ƙauyukan da ke maƙautaka da su.” Inji Noel-Berje.