Mahara sun saki daliban makarantar Kaduna 10, saura 21 cikin mutum 131 da suka sace

Shugaban kungiyar Kiristocin Najeriya, John Hayab ya bayyana cewa mahara sun saki dalibai 10 cikin dalibai 31 da suka ragd ke tsare a hannun su.

Idan ba a manta ba a watan Yuli, mahara sun sace dalibai 131 daga makarantar Bethel dake Kaduna. A hankali bayan wasu lokutta, sun rika sako daliban akai akai har zuwa ranar Asabar da suka sako mutum 10.

Hayab yace akwai sauran dalibai 21 dake tsare a hannun ‘yan bindiga.