KAR TA SAN KAR: Atiku ya taya Tinubu murnar lashe zaɓen fidda-gwanin APC

Ɗan takarar shugaban ƙasa na zaɓen 2023 mai zuwa a ƙarƙashin PDP, Atiku Abubakar, ya taya Bola Tinubu murnar lashe zaɓen fidda-gwanin APC da ya yi.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a shafin sa na Twitter, Atiku ya ce ba a banza Tinubu ya yi nasara, sai da ya ci kwakwar gwagwarmaya sosai.
“Ina taya ka murnar lashe zaɓen fidda gwani na APC. Ka sha fama kuma ka samu nasara, bayan jajircewar da ka yi.” Inji Atiku.
Tinubu ya kayar da ‘yan takara 14 sannan ya zama ɗan takarar jam’iyya mai mulki a zaɓen shugaban ƙasa na 2023 da ke tafe.
Ya samu ƙuri’u 1,271, Rotimi Amaechi ya samu 316, kuma ya zo na biyu, sai Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo ya zo na uku da ƙuri’u 235.
Bakwai daga cikin ‘yan takarar dai sun janye tare da nuna goyon bayan su ga Tinubu, tun kafin ma a fara jefa ƙuri’a.
Makonni biyu da su ka gabata Tinubu ya taya Atiku murnar lashe zaɓen fidda gwani na PDP. Kuma ya yi fatan cewa Allah ya sa su biyun ne za su yi karon-battar neman zama shugaban ƙasa a zaɓen 2023.