Wani saurayi mazaunin garin Garo, Karamar Hukumar Kabo, jihar Kano dildila wa kansa fetur ya cinna wuta saboda ya kasa biyan kuɗin jarabawar NECO.
Wasu da abin ya faru a Idon su kamar yadda Daily Trust ta ruwaito sun bayyana cewa sau uku Ɗanladi na rubutu jarabawar amma baya ci.
” Ranar da Ɗanladi zai aikata abin da yayi, sai da ya dawo wurin koyon aikin sa na kanikanci. A hanyar dawowa gida ya siyo fetur a gora ya shiga da shi ɗaki a gidan su.
Mutane sun ce sun ji ya na ihu ne a ɗaki, ya na cewa ” Jama’a a ceceni, a kawo min ɗauki. ” Daga na sai makwabta suka shiga suka kashe wutan aka wuce da shi asibiti.
Sai dai kuma rai yayi halin sa ne kwana biyu bayan an kwantar da shi a asibiti.
Wani makwabcin marigayi Ɗanladi ya shaida cewa marigayin ya taba tara rabin kuɗin amma ya kashe su saboda ya kasa samun sauran.