Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada Farfesa Attahiru Jega, tsohon Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta ƙasa (INEC), a matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami’ar Jos.
Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu, wanda ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a Abuja a ranar Alhamis, ya ce Shugaba Buhari ya kuma amince da naɗin tare da sake tura wasu shugabannin Jami’o’in gwamnatin tarayya 42.
Wasu daga cikin shuwagabannin sun haɗa da;
Jami’ar Benin- HRM Farfesa James Ortese Iorzua Ayatse.
Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓalewa, Bauchi- Oba Rufus Adeyemo Adejugbe Aladesanmi III.
Jami’ar Ahmaɗu Bello Zaria, jihar Kaduna- HM Obi Ofala Nnaemeka Alfred Achebe.
Jami’ar Alex Ekwueme daje Ndufu-Alike, jihar Ebonyi- HRM Oba Aremu Gbadebo.
Jami’ar Bayero Kano-HM, Oba Ewuare 11,
Basaraken Benin.
Jami’ar gwamnatin tarayya dake Dutse, jihar Jigawa- HRM Sarki W S Joshua Igbugburu X, Con, Ibenanawei na masarautar Bomo.
Jami’ar gwamnatin tarayya daje Gashua- HRM Farfesa Joseph Chike Edozien. CFR, Sarkin Asaba.
Jami’ar tarayya Lokoja, jihar Kogi- HRH Alhaji (Dr.) Mohammadu Abali Ibn Mohammed Idris, CON, Sarkin Fika.
Jami’ar tarayya Dutsin-ma, jihar Katsina- Sarki Dandeson Douglas Jaja Jeki, Amanyanabo na masarautar Opobo.
Jami’ar Michael Okpara, Umuduke- HRH Alhaji Abubakar Shehu Abubakar III, Sarkin Gombe.