Hisbah ta kama wasu matasa ‘yan luwadi biyar a Kano

Rundunar Hisbah dake jihar Kano ta kama wasu matasa maza biyar wanda suke kwana da juna a tsakanin su, wato ‘yan luwadi.

Shugaban rundunar Harun Ibn-Sina ya sanar da haka a wani takarda da kakakin rundunar Lawal Ibrahim ya saka hannu a a garin Kano.

Ibn-Sina ya ce sun kama wadannan matasa a garin Sheka Barde ​​dake karamar hukumar Kumbotso bayan tona asirin su da mutanen gari suka yi.

“Matasan ba su wuci yan shekara 21 ba. Mun kama su ranar 11 ga wannan wata da muke ciki.

Daga nan Ibn-Sina ya mika godiyarsa ga mutane da masu ruwa da tsaki a fanni tsaro bisa mara wa rundunar baya da suka yi.

Ya ce za su kai matasan kotu domin a yanke musu hukunci.

Ibn-Sina ya yi kira ga matasa da su nisanta kansu daga munanan aiyuka a jihar.