GUMURZUN YAƘI A DAMBOA: Yadda sojojin Najeriya su ka haka dakarun ISWAP shiga Damboa, su ka karshe fiye da 50

Dakarun ‘yan ta’addar ISWAP sun sha wuta a hannun sojojin Najeriya, lokacin da su ka yi wani mummunan shirin afkawa garin Damboa, a Jihar Barno, a ranar Laraba, 2 Ga Yuni.

Sanarwar da Kakakin Yaɗa Labarai na Rundunar Sojojin Najeriya, Mohammed Yerima ya fitar, ya bayyana cewa sojojin Najeriya sun fatattaki ‘yan ta’adda, kuma su ma kashe fiye da 50.

Ya ce sun darkaki Damboa da mummunan shiri, inda su ka nemi kai farmaki a cikin ƙatuwar motar yaƙi mai sulke da kuma motocin daukar manyan bindigogin harbo ƙananan jiragen yaki, kowace ɗauke da bindigar tashi-gari-barde.

“Akwai kuma wasu motocin maƙare da dama-bamai da nakiyoyi, sai kuma wasu garken ‘yan ta’adda a kan baruwa.”

Ya kara da cewa sojojin Najeriya sun yi masu hawan-ƙawara, inda su ka da ‘yan ta’addar ISWAP fiye da 50 zuwa barzahu.

ISWAP dai su ne hatsabiban bangaren Boko Haram da su ke balle daga Boko Haram, su ka yi wa Shekau tawaye. Daga nan su ka nemi haɗin kai da goyon bayan ISIS.

A cikin makon jiya ne rahotanni su ka cika duniya da labarin kisan Shekau a hannun ‘yan ISWAP, tare da damƙe wasu manyan kwamandojin sa da dama.

Tuni dai har sabon Babban Hafsan Najeriya, Manjo Janar Yahaya ya jinjina wa sojojin Najeriya, bisa wannan gagarimar nasara da su ka samu a kan ISWAP.

Ya kuma ƙara masu jinjina da zaburaswa cewa su ci gaba da matsa-lamba da matsa-ƙaimin ƙarasa murƙushe ‘yan ta’adda baki ɗaya.