Ɗaliban Islamiyya 136 ne aka yi garkuwa da su – Gwamnatin Neja

Gwamamnatin Jihar Neja ta bayyana cewa adadin ɗaliban Iskamiyyar da masu garkuwa su ka sace a garin Tegina na Jihar Neja, su 136 ne.

Mataimakin Gwamnan Neja, Ahmed Ketso ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke ƙarin bayani dangane da halin da ake ciki a jihar tun bayan kwashe ɗaliban da aka yi a farkon makon jiya.

Ketso ya tabbatar wa iyayen ɗaliban cewa gwamnati na yin dukkan bakin ƙoƙarin ganin an cefo ɗaliban sun koma gidajen su cikin ƙoshin lafiya.

Ya kuma yi bayanin irin motocin sintirin da gwamnatin jihar ta sai wa jami’an tsaro, har da babura.

An Haramta ‘Yan Acaba A Minna:

Domin ƙarfafa matakan tsaro a jihar, gwamnatin jihar Neja ta haramta haya da baburan achaba a cikin Minna, babban birnin Jihar Neja.

Da ya ke ƙarin bayani, Mataimakin Gwamna, Ahmed Ketso ya ce kada a ƙara ganin baburan ‘okada’ na karakaina a cikin garin Minna.

Haka su ma masu baburan kan su na hawan yau da kullum, an taƙaita zirga-zirgar su, daga ƙarfe 9 na dare zuwa wayewar gari, ƙarfe 6 na safiya.

Haka kuma gwamnati ta umarci dukkan Hakimai da Dagatai da Masu Unguwanni su tabbatar sun riƙa tantancewa, ƙididdigewa da yi wa kowane baƙon da ya sauka cikin al’umma rajistar sanin asali, tare da damƙa bayanan sa a hannun ‘yan sanda da sauran jami’an tsaron da ke da kusanci da jama’a.