Raba a Facebook
Tura zuwa Twitter
Wasu ƴan bindiga sun kashe ‘yan sanda aƙalla bakwai a wani kwanton bauna da suka kai a kusa da kauyen Zonai da ke gundumar Magami a karamar hukumar Gusau a jihar Zamfara.
Daily Trusta ta ruwaito mazauna yankin da lamarin ya faru sun ce, ƴan sandan na dawowa ne daga bakin aiki, a ranar Litinin, a wani shingen bincike da ke kusa da kauyen Zonai da ke kan titin Gusau-Magami-Dansadau, a lokacin da ‘yan bindigan suka buɗe wuta kan motar da ke dauke da jami’an tsaron.
-
Facebook
Twitter