Wasu ’yan bindiga da ake kyautata xaton masu garukuwa da mutane ne sun yi garkuwa da Sanata Dickson Imasogie, mai wakiltar mazabar Edo ta Kudu a Majalisar Dattawa.
Daily Trust ta ruwaiti an sace ɗan majalisan ne da safiyar Litinin, inda ƴan bindigan suka tare shi a kan hanyarsa ta zuwa gona a kan titin Agbor a Jihar tare da direbansa da wani mutum.
Sanatan wanda ɗan jam’iyyar PDP ne, har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto babu wani cikakken bayani da aka samu a hukumance dangane da sace shin.
An wallafa wannan Labari September 13, 2021 3:42 PM