Buhari zai lula kasar Turkiyya

Shugaba Muhammadu Buhari zai sake ficewa daga Najeriya zuwa Turkiyya, makonni biyu bayan ya dawo daga Afrika ta Kudu taron baje-koli.

Buhari zai je Turkiyya domin halartar taron haɗin guiwar ƙarfafa hulɗar cinikayya tsakanin Turkiyya da wasu ƙasashen Afrika.

Shugaba Racep Tayyib Erdogan ne ya shirya taron, bayan ziyarar da ya kawo cikin watan Oktoba a Abuja.

Za su tattauna batun ciniyakkar makamashi, tsaro, masana’antu da sauran su.

Shugaba Buhari na shan caccaka a Najeriya, inda masu adawa da yawan fitar da ke ganin cewa sagaraftu ne kawai ya ke yi da yawon gallafiri, a daidai lokacin da Arewacin Najeriya ke fama da kashe-kashen ‘yan bindiga.

Cikin wata biyu Buhari ya fice zuwa ƙasashe shida. Ya je Saudiyya, Ingila, Dubai, Scotland da kuma Afrika ta Kudu.

Yau kuma ranar Alhamis zai lula ƙasa ta bakwai, wato Turkiyya.

Jama’a da dama na ganin cewa kamata ya yi Buhari ya riƙa tura wakilcin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Yemi Osinbajo, shi kuma ya zauna ya maida hankali wajen ganin tabbatar da zaman lafiya a Arewacin Najeriya da sauran yankunan ƙasar nan.