Raba a Facebook
Tura zuwa Twitter
Rahottani sun ce rundunar sojin sama ta samun gagarumar nasara a wasu a hare haren jiragen sama da suka kai wa sansanonin ƴan fashin daji da ke jihar Zamfara da kuma Kaduna.
Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa jiragen saman sojojin sun kai hari a sansonin ƴan fashin dajin dake dajin Ƙawara a ƙaramar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna.
Wata majiyar tsaro ta ce ‘yan fashin dajin kusan hamsi ne suka hallaka a hare haren ta sama a ƙarshen mako.
-
Facebook
Twitter