Sanarwar da aka fitar a ranar Talata ta gargadi ‘yan Najeriya mazauna kasar ta Afrika ta Kudu da suyi taka tsan-tsan da irin murnar da za suyi in har Najeriya ta samu nasara a wasan na ranar Laraba.
Sanarwar ta shawarci ‘yan Najeriya masu cirani a kasar ta Afrika ta Kudu da su rika lura da kalaman da suke furtawa, sannan kuma su lura da inda suka zabi kallon wasan, musamman a wuraren taruwar jama’a.
Ta kuma roki ‘yan Najeriya da su guji murna da bukukuwan tunzura jama’a da ka iya tada zaune tsaye idan har Najeriya ta yi nasara a wasan da za a fafata a ranar Laraban nan.
A ranar Juma’ar da ta gabata ne Ademola Lookman ya zura kwallon da ta taimakawa Super Eagles samun damar tsallakewa zuwa matakin kusa da na karshe a gasar AFCON bayan ta doke Angola da ci 1-0 a wasan daf da na karshe.