ABU KAMAR WASA KARAMAR MAGANA TA ZAMA BABBA: Ahmed Lawan ya nada kwamitin Kamfen ɗin zama shugaban kasa

Shugaban majalisar Dattawa Ahmed Lawan ya naɗana mambobin kwamitin Kamfen ɗin sa.
Idan ba a manta ba Orji Uzor Kalu ya riki shugaban kasa da jam’iyyar APC a tsaida ɗan yankin Arewacin kasar a jam’iyyar APC idan ana so a yi nasara a zabe mai zuwa.
Kalu ya ce muddun APC ta tsaida ɗan kudu toh ta faɗi zaɓe warwas.
Ahmed Lawal wanda ya somo takarar kamar ba zai yi ba yanzu ya kara kaimi ya tamke ɗamarar sa tamau kanshin Aso Rock kawai ya ke ji yanzu ya ya fito da karfin sa.
yanzu ya nuna da gaske ya ke yi yanzu.
Waɗanda aka nada suna haɗa da, Femi Fani Kayode, Uzor Kalu, Barau Jibrin da dai sauran su.
Rahotanni a ranar Alhamis sun amince cewa gaba ɗaya ƴan yankin Kudu maso Gabas Ahmed Lawan za su yi.