ƘUDIRIN GYARAN ZAƁE: Sama da Sanatoci 73 sun rattaba hannun kafa sabuwar dokar zaɓe ta hanyar bijire wa Buhari -Sanata Sekibo

Sanata George Sekibo ya tabbatar da cewa akwai sama da sanatoci 73 waɗanda su ka sa hannun amincewa su tirsasa Shugaba Buhari su tabbatar da Sabuwar Dokar Zaɓe, wadda Buhari ya ƙi rattaba wa hannu domin ta zama doka.

Sekibo ya ce waɗanda suka rattaba hannun sun fito ne daga jam’iyyu daban-daban, kuma ana sa ran sake samun ƙarin wasu da dama.

Sekibo ya nuna damuwar sa a kan don me Buhari zai ƙi yarda a kafa dokar yin zaɓen-kai-tsaye na ‘yar-tinƙi a zaɓukan shugabannin jam’iyyu.

“Najeriya fa ba ƙasar mutum ɗaya ba ce, kuma ba wani kamfanin mutum ɗaya ba ne, ballantana ya ce sai abin da ya ga dama zai yi a kamfanin sa.

“Doka ta ba mu ikon kafa dokar, ko da Buhari bai amince ba, matsawar sanatoci da ke don a kafa ta sun kai kashi 2 bisa 3 na Sanatocin da ake da su 109.

“Sashe na 54 (4) da na 54 (5) ne ya bai wa sanatoci wannan ƙarfin ikon kafa dokar, duk da shugaban ƙasa bai yarda ba.”

PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa wasiƙar yin fatali da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe.

Shugaba Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da ta Tarayya wasiƙar sanar da su cewa bai yarda da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe na 2021 ba, don haka ba zai sa wa dokar hannu ba.

Fatali da ƙudirin na ciki wasiƙar da Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da ta Tarayya a ranar Talata ɗin nan, kuma majalisun biyu duk su ka karanta wasiƙun na shi a zaman ranar Talata ɗin nan.

Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan da Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ne su ka karanta wasikar ga mambobin majalisar baki ɗaya.

Dama dai tun a ranar Juma’a ne 19 Ga Nuwamba, Majalisar Dattawa ta aika wa Buhari da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe ɗin.

A cikin doguwar wasiƙar da Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ya karanta, Buhari ya bayyana dalilan sa na ƙin sa wa ƙudirin hannu don ya zama doka.

Buhari ya ce ya karɓi shawarwari daga Ma’aikatun Tarayya, Ɓangarorin Hukumomi da Cibiyoyin Gwamnati.

Daga nan ya bayyana batun kuɗaɗe da batutuwan shari’u a matsayin dalilan sa na ƙin sa wa ƙudirin hannu.

“Idan aka yi wa dokokin zaɓen kwaskwarima, to karya karsashin dimokraɗiyya kenan. Wannan kuwa shi ne ‘yancin da kowace jam’iyya mutum ya ga dama ya shiga ya zama mamba.

“Sai dai kuma a shekara mai zuwa majalisa za ta iya zaɓen hanya mafita idan an dawo daga hutun ƙarshen shekara.

Makonni biyu da su ka gabata ne wannan jarida ta buga labarin cewa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta aika wa Fadar Shugaban Kasa wasiƙar amincewa da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe