NCC ta ce kashi 50% na rumfunan zaɓen ƙasar nan ba su da intanet mai ƙarfin tura sakamakon zaɓe

Kwana ɗaya bayan da Majalisar Dattawa ta bayyana cewa ta miƙa batun amincewa da ƙudirin aikawa da saƙonnin sakamakon zaɓe ya yanar gizo ga Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC), hukumar ta ce yin hakan ba zai yiwu ba, domin kashi 50% cikin 100% na rumfunan zaɓen ƙasar nan duk ba su da ƙarfin intanet wadda za ta iya aikawa da sakamakon zaɓe ta yanar gizo.

Babban Jami’in NCC Ubale Maska ne ya bayyana halin da ya ce rumfunan zaɓen ke ciki na rashin ƙarfin intanet.

Maska ya yi bayanin a gaban Majalisar Tarayya yayin da aka gayyaci NCC ta yi bayanin shin ko tura sakamakon zaɓe ta yanar gizo.

An gayyace shi ne biyo bayan hatsaniyar da ka kaure a Majalisa, tsakanin masu goyon bayan yin amfani da yanar gizo a tura sakamakon zaɓe da waɗanda ba su goyon baya.

Maska ya ce cikin 2018 Hukumar NCC ta yi binciken gwaji a rumfunan zaɓe 119,000 a yankuna daban-daban na ƙasar nan.

“Mun gano cewa kashi 50% kaɗai a cikin su ke da ƙarfin intanet mai nauyin 3G wanda zai iya aika sakamakon zaɓe ta yanar gizo. Saura kashi 46.7 duk mai nauyin 2G gare su. Sauran rumfunan kuwa kwata-kwata babu.

“Ya kamata a sani cewa 2G ba ya iya aika sakamakon zaɓe ta yanar gizo, sai 3G.” Inji Maska.

Tuni dai ‘yan Najeriya ke ta yin tofin tir ga ‘Yan Majalisar Dattawa da na Tarayya waɗanda ba su goyi bayan yin amfani da aika sakamakon zaɓe ta yanar gizo ba.

“Ya za a ce ka cika fam ɗin neman aiki ta yanar gizo, ka aika kuɗi ta yanar gizo, a cika fam ɗin N-Power a yanar gizo, a yi rajistar NIN a yanar gizo, a cika fasfo a yanar gizo, a biya haraji a yanar gizo kuma a yi wa lambar waya rajista da yanar gizo, sannan a ce ba za a iya tura sakamakon zaɓe ta yanar gizo ba? Wannan dai maguɗi kawai ake so a yi a 2023.” Inji Ibrahim Sani a Kano.