KISAN FIYE DA MUTUM 120 A BENUWAI: Buhari ya umarci jami’an tsaro su kawo ƙarshen zubar da jinin faɗan ƙabilanci

Shugaba Muhammadu ya yi tir da mummunan rikicin ƙabilancin da ya ɓarke a cikin wasu ƙabilu a Jihar Benuwai.
Sannan kuma ya yi gargaɗin a gaggauta hana watsuwar kashe-kashen, tare da yin kira ga jami’an sojoji, DSS da ‘yan sanda su gaggauta hana ci gaban kashe-kashen.
Cikin wata sanarwar da Kakakin Yaɗa Labaran Buhari, Garba Shehu ya fitar, Buhari ya umarci a yi duk wani ƙoƙarin da za a iya yi domin a shawo kan ɓarnar. Ya ce “kashe-kashen ya yi muni.”
Akwai rahotannin da ke nuna cewa an kashe sama da mutum 80 a yankunan Umogidi da ke Entekpa-Adoka na cikin Ƙaramar Hukumar Otukpo.
Haka kuma wasu rahotannin sun tabbatar da kisan wasu mutum 34 a ƙauyen Mgaban da ke Ƙaramar Hukumar Benuwai ta Arewa a ranar Juma’a.
Shugaba Buhari ya yi tir da irin ta’addancin da ake yi a rikice-rikicen ƙabilanci.
Sannan Buhari ya umarci jami’an tsaro su gano waɗanda su ka yi kisan, su kamo su sannan su gurfanar da su a kotu, domin a hukunta su.
“Shugaba Buhari ya na taya iyalan waɗanda aka kashe jima da ta’aziyya. Kuma ya bada umarnin sake duba yadda yanayin tsaron yankin ya ke, tare da tabbatar da hakan bai sake faruwa ba.”