Hukumar FIFA Ta Zargi Kasashen Yamma Da “Munafunci” Kan Gasar Cin Kofin Duniya Ta Qatar 2022

A ranar Lahadi 20 ga watan Nuwamba ne za’a soma gasar kwallon kafa ta cin kofin duniya ta bana a Qatar, karon farko da aka fadada gasar zuwa kasashe 32, haka kuma karon farko a tarihi da za’a gudanar da gasar a yankin kasashen larabawa.