Gobara a Kasuwar Jimeta, jihar Adamawa

Daya daga cikin kasuwar Jimeta dake jihar Adamawa ta kama da wuta da yamman nan.

Wani daga cikin masu gadin kasuwan yace wutan ta fara ne bayan ‘yan kasuwa sun tashi.

Wani mazaunin kusa da kasuwan yace yanzu dai haka Jami’an kashe wuta suna kasuwan domin kashe gobaran in da wadansu kuma suke kokarin shiga kasuwan domin yin sata da sunan kawo agaji.