CBN Ya Gargadi Bankuna, Masu PoS Kan Matsalar Karancin Takardun Naira

Babban bankin ya ce yana gudanar da bincike bayan samun rahotannin da ke zargin bankunan kasar da hada kai da masu PoS wajen haifar da matsalar karancin naira, lamarin da ya ce yana shafar tattalin arzikin kasar.