Raba a Facebook
Tura zuwa Twitter
Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya naɗa tsohon mataimakin shugaban ƙasa Ambasada Babagana Kingibe a matsayin jakadan Najeriya na musamman a ƙasar Chadi da yankin Tafkin Chadi.
Wannan sanarwa na ƙunahe ne cikin wata tarda da Kakakin fadar shugaban ƙasa Malam Garba Shehu ya fitar a yammacin Litinin.
Haka zalika shugaban ƙasan ya cire shugaban hukumar bada agajin gaggawa na ƙasa (NEMA) AVM M. A Muhammad tare da maye gurbbinsa da Ahmad Mustapha Habib.
A halin yanzu, AVM M. A Muhammad shine shugaban sabuwar hukumar kula da dattawa ƴan sama da shekaru saba’in da aka ƙirƙiro.