Kungiyar kiwon lafiya ta duniya WHO ta bayyana cewa a shekarar 2021 mutum 111,062 ne suka kamu mutum 3,604 sun mutu a dalilin kamuwa da cutar amai da gudawa a Najeriya.
Kungiyar ta ce hakan ya nuna cewa Najeriya ta samu karuwa a yaduwar cutar fiye da yadda aka samu a shekarar 2020 da shekarun da suka gabata.
Wakilin WHO a Najeriya Walter Mulombo ya sanar da haka a taron inganta yin allurar rigakafin cutar da aka yi da hukumar GTFCC a Abuja ranar Litini.
Hukumar GTFCC hukuma ce dake karkashin inuwar WHO dake taimakawa wajen yaki da cutar musamman a kasashen da ya fi barkewa.
Mulombo ya yaba wa namijin kokarin da GTFCC ke yi wajen yaki da cutar a Najeriya musamman ta hanyar wayar da kan mutane mahimmancin tsaftace muhalli da ruwan da suke amfani da shi domin samun kariya daga kamuwa da cutar.
“ Hukumar ta taimaka wajen yi wa mutum miliyan 1.7 allurar rigakafin cutar a jihohin Bauchi-, Zamfara , Jigawa da Yobe.
Abubuwa 10 dake haddasa barkewar cutar a kasar nan
1. Rashin tsafta da barin ƙazanta a gida, musamman abinci da kayan abinci ko kwanukan cin abinci.
2. Zubar da tulin shara da bola aikin unguwanni, wadda ruwan sama ke maida ƙazantar ta s cikin jama’a.
3. Zubar da shara ko bola ko bayan gida a cikin ƙaramu da magudanan ruwa..
4. Yin bayan gida a fili ko a kan bola.
5. Rashin ruwa mai tsafta a cikin al’umma.
6. Ƙarancin asibitocin kula da marasa lafiya a cikin jama’a marasa galihu.
7. Ƙaranci ko rashin magungunan da za a bai wa mai cutar kwalara cikin gaggawa.
8. Matsalar ƙarancin jami’an kiwon lafiya a cikin jama’a..
9. Rashin hanyoyi masu kyau da za a garzaya asibiti da mai cutar amai da gudawa cikin gaggawa.
10. Shan ruwan ƙarama ko kogi, wanda ake zubar da shara, kashin dabbobi da kuma bayan gida.