UEFA Ta Gargadi ‘Yan Wasa Da Su Daina Gusar Da Kwalaben Abubuwan Sha

Hukumar gasar kwallon kafa ta zakarun Turai, UEFA ta bukaci ‘yan wasa da su daina kawar da kwalaben abubuwan sha da ake ajiyewa a tebur a lokacin da suke ganawa da ‘yan jarida. Hukumar ta ce kamfanonin da suke yin abubuwan sha din su na taka mihimmin rawa wajen shirya wasannin kwallon kafa.