TSADAR KAYAN ABINCI: Yadda Buhari ya nunka kasafin abincin sa na 2022, ya bar talakawa da gaganiyar neman kuɗin sayen garin masara

Matsalar ƙuncin rayuwa da tsadar kayan abinci a Najeriya ba ta buƙatar dogon bincike. Babban ma’aunin gane irin halin ƙuncin da talakan Najeriya ke ciki, shi ne nazarin kasafin abincin da Shugaba Muhammadu Buhari da Mataimakin sa Yemi Osinbajo za su lashe cikin 2022.

Kuɗaɗen da Shugaba Buhari ya ware domin sayen kayan abinci a shekarar 2022, sun nunka na 2021, sun ruɓanya na 2019, 2018. Domin na waɗannan shekaru duk ba su wuce duk shekara abincin Naira miliyan 195.5 ba.

Amma a kasafin 2022, Buhari da Osinbajo za su ci abincin Naira miliyan 457. Kun ga neman bayan sun nunka, har ma sun haura da kusan Naira miliyan 56.

Buhari ya ƙara wa kan sa da Osinbajo kuɗin sayen kayan abinci, saboda tashin farashin kayan abinci da kayan masarufi.

Ya yi wannan ƙari a lokacin da gwamnatin sa ke kukan ƙarancin kuɗaɗe, tare da yawan ciwo basussuka a ƙasashen ƙetare.

Sai dai kuma tun daga watan Maris, 2021, lokacin da farashin kayan abinci ya yi tashin da shekaru 12 a baya bai yi irin sa ba, talakawa su ka shiga cikin wani halin gaganiyar neman abin sakawa a bakin salati.

Rufe kan iyakoki ya ƙara hasala tsadar kayan abinci, ta kai yanzu talakawa shinkafar cikin gida ma na neman gagarar su, da yawa sun koma sayen niƙaƙƙen garin masara domin yin tuwo.

A lura da yadda kayan abinci ke kara tsawwala tsada. A cikin 2017 Buhari ya yi kasafin abincin Naira miliyan 115 shi da mataimakin sa. Amma a cikin 2022 zai cinye abincin Naira miliyan 301 shi kaɗai. Sai matakimakin sa na Naira miliyan 156.