Kotu ta sallami El-Zakzaky da Matar sa bayan shafe shekaru sama da 5 tsare

Babban kotun sauraran kararraki dake Kaduna ta wanke shugaban kungiyar Shiite Ibrahim El-Zakzaky da Matar sa, Zeenat dake tsare tun a shekarar 2015.

Lauyar El-Zakzaky Barista Sadau Garba, ya bayyana wa BBC Hausa cewa kotun ta wanke waɗanda ake zargin daga zargi takwas da gwamnatin Jihar Kaduna ta gabatar mata.

Wakilin mu dake Kaduna ya bayyana cewa sun ga an fice da Shehin malamin da mai dakin sa zuwa gida.