Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya ya bayyana cewa yana fatan ƴan Najeriya za su yi masa adalci idan za su tuna da shi bayan ya sauka a mulkin kasar nan.
Buhari ya faɗi haka ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga wakilin gidan talbijin din Arise.
Ya ce fatar sa shine a faɗi gaskiya, da yi masa adalci idan za a fadi abubuwan da ya yi na ci gaban kasa.