HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki cikin waɗanda suka sace a harin jirgin kasan Abuja-Kaduna Amina, ta gudanar da zangazangar gwamnati ta kara kaimi wajen tattaunawa da ƴan bindiga su saki mijinta da ke tsare a hannun ƴan bindigan.
Amina wacce ta fito ita kaɗai rike da rubutu a takarda da ke yin kira ga gwamnati su saki mijinta ta ce bata iya barci tunda ta dawo daka daji.
” Tunda aka sako ni ba na iya barci, idan na tuna mijina na can tsare a daji tare da ƴan bindiga. Don Allah ku taimake ni gwamnati ta kara kaimi wajen gqnin Maharan sun sako sauran waɗanda ke tsare a hannun su.
Amina ta ce dukkan su da ke tsare a can wurin maharan ba su da lafiya, wasu ma sun makance ba su gani, wasu sun rasa hannayen su da waau sassan jikin su saboda rashin lafiya.
Idan ba a manta ba a cikin wannan mako shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci jami’an tsaro su gaggauta sannan su ƙara ƙaimi wajen ganin an ceto sauran mutanen da ke tsare a hannun ƴan bindigan.
Garkuwa da mutane a Najeriya musamman yankin Arewa ya yi tsanani da a kullum sai an samu rahoton an sace mutane ko kuma an kashe su.
Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya umari ƴan jihar su mallaki bindigogi domin su kare kansu.