Raba a Facebook
Tura zuwa Twitter
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata 19 ga Oktoba, 2021 a matsayin ranar hutun murnar bikin Mawlidi na wannan shekarar don tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad (Sallal-lahu alaihi wa sallam).
Ministan cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, wanda ya bayyana hakan a cikin wata sanarwar a madadin Gwamnatin Tarayya da Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ta fitar, yana mai taya dukkan musulmin da ke ciki da wajen Najeriya murnar bikin wannan shekarar.
-
Facebook
Twitter