DALLA-DALLA: Guduma 7 Da Kotu Ta Buga Bisa Kan Ganduje Cikin Watan Nuwamba

A bisa dukkan alamu Gwamnan Kano Abdullahi Ganduje ya fara hango ƙarshen zangon mulkin sa na biyu, tun yanzu sama da shekara ɗaya kafin ya fita daga gidan Gwamnatin Jihar Kano.

Ganduje wanda har yau fatalwar zaɓen ‘inkwankulusib’, wanda aka ce bai kammalu ba ba ta fice daga cikin ƙwanƙwaman kan sa ba, a ɗaya gefen kuma har yau akwai kurwar zargin cushe-cushen miliyoyin daloli a kan sa.

Waɗannan fatalwa da kurwa za su daɗe a jikin sa kafin ya samu makarun da zai karya su a fitar masa da su, bayan ya sauka daga mulki, cikin 2023.

Guduma 7 Kan Ganduje:

Cikin watan Nuwamba, Gwamna Abdullahi Ganduje ya biya tarar sa da kotu ta ci har naira 800,000 saboda ya ɓata wa Ja’afar Ja’afar suna.

Ja’afar shi ne ya fallasa zargin Ganduje da aka nuno shi ya na cusa daloli aljihu.

Wannan kuɗi dai tuni har Ja’afar ya ɗora naira 200,000 a kai, sun cika miliyan ɗaya, kuma ya ce a yi ayyukan taimakawa ga mabuƙata da kuɗin.

Guduma ta biyu a kan Ganduje ita ce soke zaɓen APC ɓangaren Abdullahi Abbas da Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta yi a ranar 30 Ga Nuwamba.

Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya ce shugabannin APC ta ɓangaren tsohon Gwamna Ibrahim Shekarau ne halastattun shugabanni, a ƙarƙashin Haruna Ɗanzago.

Guduma ta uku da kotu ta ranƙwala wa Ganduje, ita ce umarnin da kotun ta bayar cewa kada ɓangaren Ganduje ya sake yin wani zaɓen shugabannin jam’iyyar APC a Jihar Kano.

Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta ɗirka wa Ganduje kulki na huɗu, inda ta haramta korar da Gwamnatin Jihar Kano ta yi wa Murabus Sarki Muhammadu Sanusi II.

Kotun ba ta tsaya nan ba sai da ta muƙa wa Ganduje kulki na biyar, inda ta ce ya biya Sanusi diyyar tauye masa ‘yanci har naira miliyan 10.

Guduma ta shida ita ce umarnin da kotun ta bayar cewa Sanusi na da ‘yancin dawowa Kano ya ci gaba da zaman sa. Ko kuma ya riƙa shigowa birnin a duk lokacin da ya ga dama.

Kotu ta ɗirka wa Ganduje guduma ta bakwai, inda ta umarce shi da ya buga roƙon neman afuwa ga Murabus Sarki Muhammadu Sanusi II a jaridu biyu na ƙasar nan.

Waɗannan batutuwa duk a cikin watan Nuwamba su ka faru, waɗanda ko shakka babu dukkan su babu wanda Ganduje zai yi farin ciki da shi. Domin tuni har ya fara gaganiyar tattara bayanan ɗaukaka ƙara.