Raba a Facebook
Tura zuwa Twitter
Sojoji tare da gudunmawar ƴan sa kai sun kuɓutar da wasu daga cikin ƴan makarantar Gwamnatin Tarayya ta garin Birnin Yawuri da aka sace a jiya Alhamis.
Rahotanni dake fitowa daga yankin Yauri da Zuru sun ce sojojin sun yi wa ɓarayin ƙofar rago ne a ranar Alhamis da daddare a tsakanin dajin Rijau da Dirin Daji.
Wasu majiyoyi sun shaidawa Hausa Daily Times cewa an kashe a ƙalla ƴan ta’adda 100 a yayin gumurzun.
Majiyoyin sun ce an yi bata kashi sosai tsakanin dakarun haɗin gwiwa na sojoji da ƴan sa kai da kuma ɓarayin dajin a ƙaramar hukumar Sakaba dake jihar Kebbi.
A halin yanzu, an bayyana cewa ɗalibai da Malaman makarantar da aka kubutar na ƙaramar hukumar Sakaba.